Рет қаралды 13,391
Gwamnan jihar Diffa a Jamhuriyar Nijar Brig. Gen. Mahamadou Ibrahim Bagadoma ya ce dole sai ƙasashen Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi sun haɗe kansu idan har suna son kawo ƙarshen matsalar tsaro a yankin tafkin Chadi.
A tattaunawarsa da wakilin sashin Hausa na RFI Ahmed Abba a yayin taron gwamnonin tafkin Chadi da ke gudana a Najeriya ya ce ko kasashe na cikin ƙungiyar ECOWAS ko ba sa cikinta to ya kamata su haɗe kansu domin yaki da matsalar tsaro.