Рет қаралды 10,645
Majalisar Wakilan Najeriya ta buƙaci shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta kafa kwamitin bincike kan yadda ake fasa gidajen yari a ƙasar. Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi tur da harin da aka ƙaddamar a Sudan da ya lakume rayukan mutane kusan 100. Shugaban Amurka Joe Biden ya gana da takwaransa na Ukraine Volodymyr Zelensky a birnin Paris kan yadda za a ci gaba da tunkarar yakin Rasha.