Рет қаралды 6,114
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan kasafin kudin Najeriya, yayin da masana tattalin arziki suka caccaki tsarin kasafin. An fara zaman makokin mako guda a jihar Filato sakamakon kisan da aka yi wa jama'a a Bokkos. Isra'ila ta yi luguden wuta a wasu yankuna na Zirin Gaza a daidai lokacin da take cewa, za ta janye wasu daga cikin dakarunta daga Gaza. Akwai hirarraki da rahotanni na musamman a cikin shirin.