Рет қаралды 16,334
Za ku iya turo naku tambayoyin zuwa ga wannan akwatun sakon namu auratayya101@gmail.com
Ga Tambyaoyin Kamar Haka:
1. Assalaamu alaikum warahmatullah wabarakatuh. Mallam ina yi maku gaisuwa da fatan alkhairi. Allah ya jikan magabata baki daya da fatan rahmarsa a garesu har damu baki daya.
Mallam menene hukuncin namijin da baya iya daukan nauyin matarsa, amma ko da yaushe yana bukatar kwanciya da ita har ma yace idan bata yarda ba Allah yana fushi da ita. Shin da gaske ne Allah ya na fushi da ita bayan ita ba'a bata nata hakkin ba ?. Allah ya yi mana rahma.
2. Assalamu alaikum warahmatullah wabarkatuhu malam ina da tambaya.tambayar ita idan mace ta haihu a wanne lokacin ya kamata ta fara sallah.
3. Assalamu alaikum malam Allah yaqarama lfy tambayata anan itace an auramun mata shekara 7 munatare yanzu haka amma, bantabajin inasanta kokadai a rainaba ko abinci tayi jinake kamar magani dan bayamun dadi, malam tsawon shekarunnan ko fuskarta bantaba karewa kalloba saboda indai zan kalleta tsanarta zata kara shiga raina amma ina kokarin bata hakkinta malam nidai Allah yagani ina cutuwa sannan nasan itama watakila tana cutuwa malam wacce shawara zakaban .