Рет қаралды 4,761
Za ku iya turo naku tambayoyin zuwa ga wannan akwatun sakon namu auratayya101@gmail.com
Ga Tambyaoyin Kamar Haka:
Za ku iya turo naku tambayoyin zuwa ga wannan akwatun sakon namu auratayya101@gmail.com
Ga Tambyaoyin Kamar Haka:
Tambaya 1
Assalaamu alaykum warahmatullah wabarakatuh. Mallam ina yi
maku gaisuwa da fatan alkhairi. Allah ya jiqan magabaata baki daya
da fatan rahmar sa a garesu har damu baki daya.
Mallam tambayana itace menene hukuncin namiji da baya daukan
nauyin matarsa (ba ci ba sha ba sutura) amma a ko da yaushe
yana bukatar kwanciya da ita har ma yace idan bata yarda ba Allah
yana fushi da ita. Shin da gaske ne Allah ya na fushi da ita bayan
ita ba'a bata nata hakkin ba?.
Tambaya 2
Assalamu alaikum,
Allah ya karawa malam lafiya da tsawon kuana.
Tambaya 1 : Matana biyu, guda na aiki, guda bata aiki. Ina so na sani : idan
inaso na temaka mata ko da kudi, ko da wani abu, ya zanyi a addinance ?
Tambaya 2 : Matana biyu, guda na aiki kuma tanada yara, guda bata aiki,
batada yara. Ni kuma ina aiki a wata qasa, kuma ina zuwa wajen su kowane
wata biyu. Ina so na sani : idan zan maido matar guda da bata aiki kuma
batada yara garin da nake aiki, ya yakamata nayi ?
Gaisuwa gareku.
Nagode,
Tambaya 3
Tambayata itace, yana inganta iyaye su raba aure. Wato su umarci
dansu namiji da ya saki matarsa kuma duk da cewa yana santa
matuka.
Nagode malam a huta lafiya