Рет қаралды 6,762
Za ku iya turo naku tambayoyin zuwa ga wannan akwatun sakon namu auratayya101@gmail.com
Ga Tambyaoyin Kamar Haka:
Tambaya 1
Assalamu alaikum, malam ina yini , Allah ya taimaka. Malam naga
wani wa'azinka da kace idan aka tilastawa miji ya rabu da matarsa
ba da son ranshi ba, to bata saku ba to kuma hakan ya faru dani
mijina aka tilastawa masa ya sakeni bada son ranshi ba kuma
muna son juna harma muna da yara biyu, gashi harna sake wani
aure inada cikin wata 3, shin ya matsayin aurena na yanzu, yaya
kuma matsayin aurena nada.?
Tambaya 2
Assalam alaikum malam akwai yarinyar da na tura neman aurenta
amma daga tambaya babanta ransa ya baci, har yana zai dauki
mataki akaina shi bazai mata aure ba karatu zatayi kuma itama
tanason auren kuma nace zan dauki nauyin karatunta tayi agidana
kuma yanzu ne daidai ya kamata aurenmu saboda shakuwarmu
kuma inada sana’a sannan kuma shima mamanta lokacin da sukai
aure dashi agidansa ta karasa secondary amma ita yarsa yace sai
tayi likita. Malam nida yarinyar duk muna cikin yanayi ita tana
makaranta batajin dadin karatun saboda maganar da yayi nima
wajen sai ahankali jiya ko patient daya bangani ba ni likita ne
saudia nakeso tazo muzauna. Malam wallahi dayasan yanda zan
kula masa da ita kuma nake sonta bazaimin haka ba abani
shawara.
Tambaya 3
Assalamu alaikum, Malam mijina yana da ciwon sugar baya iya
gamsar dani muna ta hakuri a haka shine yake shirin kara aure da
nayi mashi magana sai yace shi sai yayi naje in fada mata halin da
yake ciki ni Kuma bazan iya ba. To malam ana kara aure alhalin
wadda take gida hakuri take akan hakkinta? Malam ni na fara
shawara in fita daga gidan in samu wani tunda shi kanshi kadai ya
sani. Don Allah a bani shawara Nagode