Рет қаралды 12,867
Masu son aiko da nasu tambayoyin sai su tura su zuwa ga akwatun Sakonmu Kamar Haka auratayya101@gmail.com.
Ga Tambayoyin Kamar Haka:
1. Assalamu alaikum Malam, ALLAH ya Kara ilimi mai albarka da Karin
fahinta. ALLAH yakara lafiya YA HAYYU YA QAYYUM.
Malam a Wani karatun ka naji kace a rabawa mata gida, ma'ana
kowacce ta zabi gidanta. Wani lokacin naji kamar kace matan sai sun
yadda in ba haka ba baza a hadasu ba. To ni Malam nayi Hakan
Amma kullum cikin zargi nake . Da na sayi Wani Abu ko na Kai Wani
abun can. Saboda haka na yanke hukuncin hadasu wuri Domin
kowacce take ganin abin da nake baiwa yar uwarta na huta da zargi,
to itakuma uwargida taki Kuma itace mai zargin. Kullum tana
kawomin karatunka. Malam menene shawara? Nagode wassalam.
2.Assalamualaikum warahmatullahi wabarrakatuhu.
Malam inason ayimin bayani akan hukuncin
1. raba iyali ko wacce da gidan ta. Acikin mabanbantan gurare
2. Wacece zaka baiwa Daman zabi zuwa garin da kafi zama aciki,
kodai uwar gida ta zauna inda take amarya Kuma a tafi da
ita? Nagode.