Рет қаралды 9,104
Birnin Faaz na kasar Morocco na daya daga cikin wurare muhimmai da mabiya darikar Tijjaniyya a fadin duniya ke son kai ziyara, saboda a can ne hubbaren shugaban darikar na farko, Sheikh Ahmadu Tijjani yake.
Tafiya ce ta sa’a uku zuwa da rabi a jirgin kasa, a mota kuma sa’a hudu da doriya za ta kai ka birnin mai nisan kilomita 387 daga Rabat babban birnin kasar.
Tun kana ganin gine-gine a hanya har sai ka fara ganin hamada tsagwaronta.