Рет қаралды 1,156
GWAMNAN JIHAR KANO YAKAI ZIYARAR BAZATA MATATAR RUWA DAKE TAMBURAWA.
A Kokarin Gwamnatin jihar Kano Karkashin Jagorancin Hazikin Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf Dan ganin tasamawa Al, umar jihar Kano Tsaftataccen ruwan famfo kuma ishashshe, Ayammacin wannan rana ta juma'a Mai Girma Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf yakai Ziyarar bazata Babbar matatar ruwansha dake tamburawa Dan ganewa idansa halin da wannan tasha ta ruwa take cikin duba da wani Dan yanayin karancin rashin ruwa da ake fuskanta awasu yankuna dake cikin birnin kano.
Yayin Wannan ziyara Gwamnan ya bayyana rashin jindadinsa dan ganeda halin karancin ruwan sha da ake fuskanta awasu yankuna dake cikin wannan jiha, inda Gwamnan yakara da cewa cikin ikon Allah Gwamnatinsa zata dukufa da aiki babu dare babu rana Dan ganin Al,umar jihar nan sun cigabada samun ishashshen ruwan sha kuma Mai tsafta a dukka fadin jihar Kano.