Рет қаралды 12,575
Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan da ke birnin Kano a Najeriya, Sheikh Abdullahi Uwaisu Mohammad Abba, ya ce akwai bukatar kawo gyara a tsarin koyarwa a makarantun zaure saboda "rayuwa na kara fadada kuma mutane sun kara yawa".
Malamin ya bayyana hakan ne a cikin shirin Ku San Malamanku na BBC Hausa wanda yake tattaunawa da malaman addini kan rayuwarsu.