Рет қаралды 1,625
1. Kamfanonin Faransa na ficewa daga Nijar bayan da sojojin juyin mulkin suka nemi raba gari da Faransar, sai dai masana na gani hakan wata dama ce ga kasar domin murmurewa.
2. Sama da masana'antu 767 sun rufe kofofinsu a Najeriya sannan wasu 300 sun fada cikin matsala, lamarin da ya haifar da karuwar zaman kashe wando.
3. Tsohon shugaban Najeriya Cif Olusegun Obasanjo ya bayyana bukatar kasashen Afrika su fito da tsarin dimukurdiyya da ya dace da nahiyar domin samar da mafita zama ga kalubalen rashin ci gaba.
4. A Kamaru dubban mutanen da rikicin yankin rainon Ingilishi ya raba da gidajensu sun zargi hukumomin kasar da watsi da yanayin kuncin da rikici ya jefa su.
5. Yayin da ya rage kwanaki 100 a fara gasar cin kofin nahiyar Turai Euro 2024 wanda Jamus za ta karbi bakunci za a ji kalubalen da ke gaban kasar.