Рет қаралды 2,254
Iyayen Malam Khuzaima Isma'ila Idris bin Sulaiman, Ardo Abdullahi asali mutanen Jahun ne, daga bisani suka koma Jihar Bauchin Najeriya.
Amma shi Malam Khuzaima an haife shi ne a garin Jos a unguwar Dodo. Ya fara neman ilimi daga wurin mahaifinsa na addini da boko.
Ya yi karatun addini a wajen yayarsa mai suna Basma, saboda girma da rashin lafiya da ta samu mahaifinsu, wanda ya sanya ba zai iya ci gaba da koyar da su ba.
Ya samu sakafa sosai a hannun mahaifinsu da ya tarbiyyantar da su a kan cewa karatu nishadi ne, yana yawan zama da yammaci a kofar gida inda yake rera koyar da su wakokin Shehu Usman Dan Fodio cikin harshen Larabci da Filatanci.