Рет қаралды 1,294
Barkanmu da rana. Shirinmu na karfe biyu agogon Najeriya da Nijar, tare da Abdullahi Tanko Bala ya yi muku tanadin wadannan rahotanni:
Gwamnatin Najeriya ta ce za ta daina yin afuwa ga jami'an da ake samu da hannu wajen kwashe dukiyar kasa.
An shiga mawuyacin hali a birnin Maiduguri na jihar Borno bayan fashewar babbar madatsar ruwa ta Alau da ta haddasa ambaliyar ruwa a cikin unguwanni da dama. Yayin da ake fargabar an samu hasarar rayuka da dukiyoyi, hukumomi sun dauki matakai na agajin gaggawa.
Daga kasar Chadi ma dai batun ambaliyar ruwan ce ta haddasa asarar rayukan sama da mutum 300, sannan gidaje da dama sun ruguje.
Shekara guda bayan da mummunar ambaliyar ruwa ta afka wa kasar Libiya, al'ummar kasar na kokarin murmurewa daga iftila'in tare da fatan ganin an sake gina yankin Derna da tuni yakin basasar kasar ya durkusar.