Рет қаралды 9,978
Sama da fursunoni 100 sun tsere daga gidan yari Suleja da ke Najeriya bayan katangarsa ta fadi sakamakon ruwan saman da aka tafka. Ƙungiyoyin kare hakkin bil'adama sun zargi sojojin Burkina Faso da yi wa fararen hula 200 kisan gilla. Amurka ta bi sahun Majalisar Dinkin Duniya da Ƙungiyar Tarayyar Turai wajen ganin an gudanar da bincike kan ƙaburburan da aka gano makare da gawarwaki a Zirin Gaza, inda ake zargin Isra'ila da hannu.